Reader ready.
A Brief Introduction to Islam (Article - Hausa)
A book in Hausa makes a brief introduction to Islam religion showing its comprehensiveness of all fields of life, along with explaining the six pillars of the Islamic faith.
Contributors
AuthorsScientific Research Admission of Islamic University , Madinah Munawara
Sourcesiu - The Islamic University Website in Almadinah Almunawara
Download all material files
2 files • 898 KB
Material files
1 / 2Social-friendly share text
Zan yi farin ciki in raba wannan da kai:
📄 DA SUNAN ALLAH MAI MATUKAR RAHAMA DA MATUKAR JIN KAI TAKAITACCEN BAYANI GAME DA MUSULUNCI (Hausa)
📝 تعريف موجز بالإسلام بلغة : الهوسا Introduction to Islam in Hausa Language DA SUNAN ALLAH MAI MATUKAR RAHAMA DA MATUKAR JIN KAI TAKAITACCEN BAYANI GAME DA MUSULUNCI Dukkanin godiya ta tabbata ga Allah; Ubangijin talikai, sannan salati da taslimi ga shugaban manzanni; Annabinmu MUHAMMADU, hada da gabadayan alayensa da sahabbansa. Bayan haka. Shi dai MUSULUNCI, shi ne sakon Allah na karshe - daga jerin sakwanninSa - zuwa gabadayan al'umma, wanda Ya saukar da shi ga cikamakon annabawanSa; MUHAMMADU DAN ABDULLAHI, tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi. MUSULUNCI shi ne addinin gaskiya wanda Allah ba Ya karbar wani addini daga wani mahaluki in ba shi ba. Kuma, hakika Allah Ya sanya shi addini sassauka da ba wata wahala a cikinsa; don bai wajabtawa mabiyansa abin da ba za su iya ba, bai kuma dora masu abin da ya fi karfinsu ba. Hakanan, MUSULUNCI addini ne da kadaita Allah ne tushensa, rahama ruhinsa, gaskiya takensa; ya tsaya a kanta tsayin-daka, kamar yadda ya ke cike makil da adalci, zuwa gareshi yake kira, kuma a kansa yake kaiwa yake komowa. Harwalau, MUSULUNCI shi ne addinin nan mai girma wanda yake fuskantar da bayin Allah zuwa ga duk wani abu mai amfani a garesu a addininsu da duniyarsu, yake kuma gargadinsu daga duk wani abin da yake mai cutarwa ne a garesu a addininsu da rayuwarsu. Haka zalika, MUSULUNCI shi ne addinin da Allah Ya gyara akidu, da halaye, da rayuwar duniya da ta lahira da shi. Da kuma shi ne ya gyara tsakanin soye-soyen ran da suke a rarrabe, da zukatan da suke nesa da juna. Ta haka ne ya tseratar da su daga duffan bata zuwa hasken shiriya, ya kuma yi masu ja-gaba zuwa hanya madaidaiciya. Sannan - bayan dukkanin abubuwan da suka gabata - MUSULUNCI shi ne tsayayyen addini, wanda aka kyautata shi matuka gaya cikin kafatanin labarurrukansa, da daukacin hukunce-hukuncensa. Babu wani labari da ya bayar sai da gaskiya, kuma ba bu wani hukunci da ya yi sai da alheri da adalci, daga ingantattun akidu, da kyawawan ayyuka, da halaye mafifita da ladubba madaukaka. MANUFAR SAKON MUSULUNCI Manufar sakon musulunci ita ce tabbatar da wadannan abubuwa: (1) Sanar da mutane Ubangijinsu (mahaliccinsu) ta hanyar ilmantar da su sunayenSa wadanda suke iyaka ne wajen kyau, da sifofinSa wadanda suke sun kai kololuwa wajen daukaka, da ayyukanSa cikakku. (2) Kiran bayin Allah zuwa bautar Allah Shi kadai, ba shi da abokin tarayya (wato su aikata abubuwan da ya wajabta masu su kuma bar wadanda ya hane su) . Kuma wannan bauta ce kadai za ta gyara masu duniyarsu da lahirarsu. (3) Tunatar da su halinsu, da makomarsu bayan mutuwarsu, da kuma abubuwan da za su gamu da su a kaburburansu, da kuma lokacin tashinsu daga cikinsu ranar kiyama suna rayayyu, hada da lokacin yi masu hisabi, da kuma tuna masu makomarsu cewa dayan biyu ce: ko dai aljanna ko wuta. GINSHIKAN MUSULUNCI Ginshikan musulunci da suka fi muhimmanci a takaice su ne: GINSHIKI NA FARKO: AKIDA Wato imani da jiga- jigan imani guda shida: JIGO NA FARKO: IMANI DA ALLAH Wannan kuma ya kunshi abubuwa masu zuwa: (1) IMANI DA RUBUBIYYAR ALLAH Wato imani da cewar ba wani ubangiji, mahalicci, mamallaki, mai gudanarwa da sarrafa al'amuran bayinsa sai shi. (2) IMANI DA ULUHIYYAR ALLAH Wato imani da cewa Shi kadai ne abin bauta na gaskiya; duk wani abin bauta ba shi ba, karya ne. (3) IMANI DA SUNAYEN ALLAH DA SIFOFINSA Wato imani da cewa tabbas Allah Yana da sunaye masu matukar kyau, da cikakkun sifofi masu matukar daukaka, a tabbatar masa da su kamar yadda suka zo a Al-Kur'aninSa da sunnar manzonSar. JIGO NA BIYU: IMANI DA MALA'IKUN ALLAH Mala'iku manyan bayi ne da Allah Madaukakin Sarki Ya halicce su, Ya kuma dora masu ayyuka daban-daban, su kuma suka mika wuya gareshi, suna masu yi masa biyayya, kamar yadda suke bauta masa ba-dare-ba-rana. Daga cikin wadannan Mala'iku akwai: 1- JIBRILU, wanda aka wakilta wajen sauko da wahayi, yana sauko da shi daga Allah zuwa wanda Allah din Ya so na daga AnnabawanSa da ManzanninSa. 2- MIKA'ILU; wanda a ka wakilta wajen ruwa da tsirrai. 3- ISRA'FIL...
🔗 https://b.islamhouse.com/ha/articles/587