Reader ready.
NI MUSULMI NE (Article - Hausa)
NI MUSULMI NE RUBUTAWAR DR. MUHAMMAD IBN IBRAHIM AL-HAMAD. Ni musulmi ne, wannan yana nufin cewa Addini na shi ne Musulunci,Musulunci kalma ce mai girma abar tsarkakewa, Annabawa - aminci ya tabbata a garesu - sun gajeta ne tun daga na farkonsu zuwa na ƙarshensu;Wannan kalmar tana ɗaukar wasu ma'anoni maɗaukaka da darajoji manya;Suna nufin miƙa wuya, da jawuwa da biyayya ga Mahalicci,Suna nufin aminci, da zaman lafiya, da arziƙi, da amintuwa, da hutu ga mutum ɗaya da kuma taron jama'a. Saboda haka kalmomin aminci da Musulunci suna daga mafi yawan kalmomi a zuwa a cikin Shari'ar Musulunci;Aminci suna ne daga sunayen Allah,Kuma gaisuwar musulmai a tsakaninsu ita ce Aminci,Gaisuwar 'yan Aljanna ita ce (Salam),Musulmi na gaskiya shi ne wanda musulmai suka kuɓuta daga harshensa da kuma hannunsa;Musulunci shi ne Addinin alheri ga mutane baki ɗaya; yana yalwatar da su, kuma shine hanyar tsiran su a duniya da lahira;sabo da haka ne ya zo mai cikawa mai tattarowa mai yalwatawa mai bayyanawa, buɗaɗɗe ga kowane mutum, ba ya banbance asali akan wani asalin, ko wani launi a kan wani launin, kai yana duba ga mutane duba ɗaya,Kuma wani baya banbantuwa a cikin Musulunci sai da gwargwadon riƙonsa ga koyarwarsa. Saboda haka ne dukkan rayuka madaidaita suka karɓe shi; domin cewa shi mai dacewa ne ga ɗabi'ar da aka halicci mutum a kanta;Kowane mutum ana haifar sa abin ɗabi'antarwa a kan alheri, da adalci, da 'yanci, mai son Ubangijinsa, mai tabbatarwa da cewa shi abin bautawane ga macancancin ibada Shi kaɗai banda waninSa;Kuma ba wanda zai juya daga wannan ɗabi'ar da aka halicci mutum a kanta sai dai da wani abu mai juyarwa da zai canza ta,Wannan Addinin Mahaliccin mutane Ya yarda da shi, kuma Ubangijinsu, kuma Abin bautarsu. Addinina shi ne Musulunci yana koyar da ni cewa zan rayu a cikin wannan duniyar, bayan mutuwa ta zan koma zuwa wani gidan da ban, shi ne gidan wanzuwa wanda makomar mutane take kasancewa a cikinsa, ko dai zuwa Aljanna, ko zuwa wuta. Addinina shi ne Musulunci, yana umarta ta da umarce-umarce, kuma yana hanani daga hane-hane;Idan na tsaya tsayin daka da waɗancan umarce-umarcen, na kuma nisanci waɗancan hane-hanen, na tsira a duniya da lahira,Idan na yi sakaci a cikinsu taɓewa za ta tabbata a duniya da lahira gwargwadon sakacina da taƙaitawata. Mafi girman abin da Musulunci ya umarce ni da shi shine kaɗaita Allah;Ni ina shaidawa, kuma ina ƙudirewa kudircewa a yanke lallai cewa Allah Shi ne Mahallicina, kuma abin bautata;Ba zan bautawa kowa ba sai Allah, don so gareShi, da kuma tsoro daga uƙubarSa, da kwaɗayi ga ladanSa, da kuma dogaro a gareShi,Wannan Tauhidin yana kamantuwa ne da shaidawa ga Allah da kaɗaitaka, kuma ga AnnabinSa Muhammad da Manzanci;Muhammad shi ne cikamakin Annabawa, Allah Ya aiko Shi don ya zama rahama ga talikai, kuma Ya cika Annabci da Manzanci da shi, don haka babu wani Annabi a bayansa,Haƙiƙa ya zo da wani Addini mai gamewa, mai ingantuwa ga kowane zamani, da wuri, da al'umma. Addinina yana umarta ta da umarni a yanke da yin imani da Mala'iku, da dukkanin Annabawa, musamman ma na gaba-gabannsu: Nuhu, da Ibrahim, da Musa, da Isa, da Muhammad - amincin Allah ya tabbata a garesu -. Kuma yana umarta ta da yin imani da littattafan sama waɗanda aka saukar ga Manzanni, da bin na ƙarshensu, kuma cikamakinsu, kuma mafi girmansu shi ne (Al-ƙur'ani mai girma). Addinina yana umarta ta da yin imani da ranar ƙarshe, wacce za'a yi wa mutane sakayya a cikinta a kan ayyukansu,Kuma yana umarta ta da yin imani da ƙaddara, da yarda da abin da yake kasancewa gareni a wannan rayuwar na alheri da sharri, da ƙoƙarin tafiya a cikin riƙo da sabubban tsira. Imani da ƙaddara yana ba ni hutu, da nutsuwa, da haƙuri, da barin da na sani a kan abin da ya wuce؛Domin cewa ni na sani sani na yaƙini cewa abin da ya same ni bai kasance zai kuskure min ba, kuma abin da ya kuskure min bai kasance zai same ni ba;Dukkanin wani abu abin ƙaddarawa ne, kuma abin rubutawa ne daga Allah, ba abin da ke kaina sai dai riƙo da sabubba, da yarda da abin ...
Material files
1 / 1